1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Tarzoma ta tashi bayan zaben Nijar

Mouhamadou Awal Balarabe
February 25, 2021

Tarzomar bayan zabe da ta barke a Jamhuriyar Nijar bayan nasarar Bazoum Mohamed na PNDS-taryya ta yi sanadiyyar mutuwar wani jami’i, lamarin da ya sa hukumomi daukan matakan a kan wadanda ake zargi da marar hannu a boren

https://p.dw.com/p/3pvqn
Bildkombo I Präsidentschaftswahlen in Niger qualifiziert haben: Mohamed Bazoum und Mahamane Ousmane

Watsi da sakamakon zagaye na biyu na zaben shugaban kasa da Mahamane Ousmane dan takarar adawa ya yi, ya haddasa tashin hankali a Yamai babban birni da wasu garuruwa na Jamhuriyar Nijar. Magoya bayan 'yan adawa sun yi bore ko da shi ke hukumomi sun kwantar da kurar rikicin tare da kame wasu kusoshin 'yan adawa da ake zargi da hura wutar rikicin. A mafi yawan lokuta dai, wanda ya sha kaye ya saba kalubalantar sakamakon zaben shuganan kasa a Nijar.

Tsallake zuwa bangare na gaba Rahotanni da Sharhuna