1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaGabon

Yawan Juyin mulkin sojoji a Afirka

August 30, 2023

Da sanyin safiyar ranar Laraba ne sojojin kasar Gabon da ke a tsakiyar Afirka, suka sanar da kifar da gwamnatin farar hula, bayan kammala zaben kasa da aka yi.

https://p.dw.com/p/4VjWe
Sanarwar juyin muli a Gabon
Hoto: Gabon 24/AFP

Sojojin da suka fito ta kafar talabijin, sun bukaci kowa da kwantar da hankali a kasar, suna mai bayyana himmatuwarsu ga girmama manufofin Gabon da ta kasa-da-kasa.

Cikin jawabin da ya gabatar guda daga cikin sojojin ya ce sun soke zaben da hukumar zabe ta sanar da shugaba mai ci Ali Bongo a matsayin wanda ya yi nasara da kundin tsarin mulki da majalisun dokokin kasar da ma sauran hukumomin gudanarwa a Gabon.

Gwamnatin Gabon din dai ta sanar da kafa dokar hana zirga-zirga a fadin kasar baya ga katse hanyoyin sadarwar Intanet da aka yi

Duk wani zabe da aka gudanar a kasar mai arzikin Mai, na karewa ne da rigingimu tun a shekarar ta 1990 da ta koma tsarin jam'iyyu barkatai na siyasa.

Tsallake zuwa bangare na gaba Rahotanni da Sharhuna

Rahotanni da Sharhuna