1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
Salon rayuwaAfirka

Yan gudun hijirar Chadi na son fara noma a Afirka ta Tsakiya

Jean-Fernand Koena Rakia Arimi/Mouhamadou Awal
February 9, 2024

'Yan gudun hijirar Chadi da ke a arewacin Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya na neman filayen noma domin gudanar da harkokinsu. Hukumar kula da 'yan gudun hijira ta MDD da hukumomi sun fara tattaunawa don biyan wannan bukatar.

https://p.dw.com/p/4cDwl
'Yan gudun hijira na neman na sawa a bakin salati
'Yan gudun hijira na neman na sawa a bakin salatiHoto: Marie-Helena Laurent/WFP/AP/picture alliance

A yankunan Bétoko da Bédaka da ke cikin jihar Paoua a arewacin Jamhriyar Afirka ta Tsakiyya,  'yan gudun hijira da suka fito daga kasar Chadi na neman izinin yin amfani da fillayen noma. Marina da ke zaman daya daga cikin 'yan gudun hijira ta ce: " Babban burinmu shi ne, mu tsara kanmu gungun-gungu na noma idan aka samar mana da filayen noma da kayan aiki : Hakan zai ba mu damar cin gashin kanmu tare da kare mutuncinmu da kuma daidaito a wannan duniya da rashin gaskiyya ya yi yawa''

Karin bayani: Sauyin yanayi ya shafi 'yan gudun hijira

Kusan 'yan gudun hijira 31,000 da suka fito daga kudancin Chadi ne ke zaune a jihar ta Paoua bayan da suka guje wa rikicin makiyaya da manoma . Jacqueline Kornandji da ta samu mafaka a jihar bayan da ta a rasa mijinta a tashin hankali ta ce: "Kannen  mijina na gona domin kula da ita. Amma a ranar da misalin karfe biyu na rana, wasu Larabawa suka kewaye su, kafin su kashe daya daga cikinsu da adduna. Da mijina ya samu labari, sai ya je wurin da abin ya faru. shi ma aka yi masa kwanton bauna aka kashe shi. Gwamnatin Chadi na da hannu a kan a abin da ya faru "

'Yan Chadi da dama sun kaurace wa matsugununsa sakamakon hare-haren ta'addanci
'Yan Chadi da dama sun kaurace wa matsugununsa sakamakon hare-haren ta'addanciHoto: Jerome Delay/AP/picture alliance

Karin bayani: Rayuwar 'yan gudun hijira a Zambiya

Jacqueline na son ci gaba da ayyukan noma a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya. Amma kafin ta samu izini daga hukumomi, a yanzu ta bude wani dan karamin wurin sayar da abinci.  Saboda haka ne Olivier Fafa Attidza,  wakilin hukumar  kula da 'yan gudun hijira yake kokarin kwantar musu da hankula. Ya ce: " Muna goyon bayanku. Za mu yi duk kokarinmu domin kai namu goyon baya ga hukumomi da al'ummar Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya domin taimaka muku duk tsawon kasancewarku nan."

Karin bayani: 'Yan gudun hijira na Sudan a Chadi

Filayen noma na da matikar mihimmanci a kewayen tafkin Chadi
Filayen noma na da matikar mihimmanci a kewayen tafkin ChadiHoto: DW

A garuruwan  Bétoko da Bédaka, yawancin jama'a na daogara ne galibi da aikin gona. A yanzu kokarin da ake yi shi ne, na yin rigakafi ga afkuwar rigingimu tsakanin manoma da makiya: Shi ya sa hukumar 'yan gudun hijira ta MDD ke ci gaba da tattaunawa da al'umma domin samun fahimtar juna a kan batun rabon filayen noma ta yadda ko mai zai tafi lafiya ba tare da an samu tashin hankali ba.

Karin bayaniMatsalolin 'yan gudun hijira a Sakkwato

Justin Malekian da ke da zama garin Paoua ya ce: " Hukumar da ke kula 'yan gudun hijirar da gwamnati za su iya shiga tsakani don nemo filiye, saboda matsalar fili ce ke haifar da rikici tsakanin 'yan gudun hijira  da jama'a a gari. A wannan matakin ne ya kamata hukumomi su mayar da hankali sosai domin a samu isasshiyar mafita mai dorewa."

'Yan gudun hijirar sun gamsu da irin karbar da al'ummar yanki Paoua suka yi musu, inda suka tabbata cewar rayuwarsu za ta samu sauyi kuma za su samu biyan bukata cikin girma da mutunci.