1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Janar Tchiani ya rusa majalisun jihohi da na yankuna

Abdoulaye Mamane Amadou Abdourahmane Hassane
April 5, 2024

Shugaban gwamnatin mulkin sojan Nijar Janar Abdourahamane Tchiani, ya kori shugabannin kananan hukumomi da na majalisisun jihohi da yankunan kasar.

https://p.dw.com/p/4eS4p
Shugaban majalisar mulkin sojan Nijar Abdourahmane Tchiani da mukarabansa
Shugaban majalisar mulkin sojan Nijar Abdourahmane Tchiani da mukarabansaHoto: Balima Boureima/picture alliance/AA

A cikin wata dokar mai dauke da sa hannun shugaban da aka karabnta a kafar talabijin din kasar Janar Tchiani ya rusa majalisun mashawartan da ke rike da mukaman ne tun a shekarar 2020, ba tare da wani karin haske kan dalilan gwamnatinsa na daukar matakin ba.

Karin bayani : Kotu ta umarci sojojin Nijar su saki dangin Bazoum

Tuni ma dai shugaban ya dauki matakin maye gurbisu da wasu galibi sojoji da 'yansanda da wasu daidaikun fararen hula galibi masu alaka da sojojin da ke jan ragamar mulki.

Karin bayani : Niger na kara daukar matakai a kan Faransa

Wasu manya-manyan biranen kasar ciki har da Yamai da ke karkashin jagorancin wani kusa a jam'iyyar Hama Amadou, a yanzu zai kasance ne karkashin jagorancin soja in ji sanarwar da aka karanta a kafar yada labarun gwamnati.