1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaGabas ta Tsakiya

Iran ta yi tir da harin Amurka da Burtaniya suka kai Yemen

Abdulkarim Muhammad Abdulkarim
February 25, 2024

Tun bayan fara yakin Gaza ne 'yan tawayen Houthi suka fara kai hari kan jiragen ruwan da ke bi ta Baharmaliya, a matsayin martani, inda suka yi alkawarin ci ga da kai hari kan jiragen har sai an dakatar da yakin Gaza

https://p.dw.com/p/4crc4
Hoto: Mohammed Hamoud/Anadolu/picture alliance

Kasar Iran ta yi allawadai da hare-haren da Amurka da Burtaniya suka kai Yemen, inda ta ce wannan kokarin haddasa rincabewar rikicin ne kawai a yankin.

Karin bayani:Amirka ta lalata makaman 'yan Houthi a tekun Bahar Maliya

Wannan na cikin sanarwar da mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Nasser Kanani ya fitar a Lahadin nan, kamar yadda kamfanin dillancin labaran Faransa AFP ya rawaito, yana mai kokawa da yadda manyan kasashen biyu suka gaza yin katabus wajen dakatar da yakin Gaza.

Karin bayani:Amurka da Burtaniya sun kai sabbin hare-hare Yemen

Tun bayan fara yakin Gaza ne 'yan tawayen Houthi suka fara kai hari kan jiragen ruwan da ke bi ta Baharmaliya, a matsayin martani ga yakin, inda mai magana da yawunta Yahya Saree ke ba da tabbacin ci gaba da ka wa jiragen farmaki har sai an dakatar da yakin Gaza.