1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaGabas ta Tsakiya

Amurka da Burtaniya sun sake kai hari Yemen

February 4, 2024

Amurka da Burtaniya sun sake kai jerin hare-hare a wadansu cibiyoyin 'yan Houthi da ke Yemen a matsayin martani ga hare-haren da 'yan tawayen masu alaka da Iran ke kai wa jiragen ruwa a Tekun Maliya.

https://p.dw.com/p/4c1Tj
Amurka da Burtaniya sun sake kai hari Yemen
Amurka da Burtaniya sun sake kai hari YemenHoto: U.S. Central Command/Handout via REUTERS

A cikin wata sanarwar hadin gwiwa Amurka da Burtaniya sun ce sun kai wadannan hare-hare a ranar Asabar 03.02.2024 a kan mabuyar 'yan tawayen Houthi 36 a wurare 13 da ke kasar Yemen la'akari da ci gaba da tarnakin da 'yan tawayen ke kawo wa zirga-zirgar jiragen ruwa na kasa da kasa da na kasuwanci da kuma jiragen ruwan yaki masu ratsawa ta Tekun Bahar Maliya.

Karin bayani: Amurka da Burtaniyya sun kai harin bama-bamai kasar Yemen kan 'yan tawayen Houthi

Jim kadan bayan sabbin hare-haren kakakin 'yan tawayen na Houthi Nasr al-Din Amer ya wallafa cewa muddin ba a samar da zaman lafiya a Gaza ba, ba za su bari kwanciyar hankali ta yalwata a yankin ba.  

Karin bayani: 

Samamen hadin gwiwar da ke zama karo na uku da kasashen kawaye ke kai wa 'yan Houthi na zuwa ne washegarin hare-haren daukar fansa da Amurka ta kai a Iraki da Siriya kan mutuwar sojojinta uku a kudancin kasar Jordan a ranar 28 ga watan Janairu.