1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Bello Matawalle na dab da shiga komar EFCC

May 19, 2023

Al'ummar jihar Zamfara da ma kungiyoyin fararen hula na ci gaba da martani kan cece-kucen da ake tsakanin gwamnan jiha Bello Matawalle da hukumar EFCC.

https://p.dw.com/p/4Rb3x
Najeriya | Zamfara | Bello Matawalle
Gwamnan jihar Zamfara Bello MatawalleHoto: Zaharaddeen Umar/DW

Hukumar Hana Almundahana da Kudin Al'ummar Najeriyar EFCC, ta ce tana gudanar da bincike a  kan badakalar kudi fiye da naira billiyan 70 da take zargin gwamnan Zamfara Bello Matawalle da hannu dumu-dumu a ciki. Koda yake shi ma Gwamna Matawalle ya kalubalanci hukumar ta EFCC, inda ya ce ya kamata shugaban hukumar Abdulrashid Bawa ya ajiye nasa aikin na wani lokaci, domin shi ma a gudanar da bincike kansa dangane da zargin rashawa da ake masa. Ra'ayoyin al'ummar jihar ta Zamfara da ke zaman guda cikin jihohi mafiya talauci a Najeriyar dai ya bambanta, inda wasu ke goyon bayan Gwamna Matawalle wasu kuma ke ganin lallai akwai bukatar gudanar da bincike kan yadda gwamnatinsa ta tafiyar da kudin al'ummar jihar a tsawon shekaru hudun da ya kwashe yana mulki. Da ma dai hukumar ta EFCC ta sha alwashin cafke wasu gwamnoni da ta ce tana zarginsu da al'mundahana da kudin al'umma, a ranar 29 ga wannan wata na Mayu da muke ciki. A wannan ranar ce dai za a mika mulki ga sabuwar zababbiyar gwamnati a Najeriyar, inda shugaba Muhammadu Buhari da wasua gwamnonin kasar za su sauka daga kan madafun iko.