1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Yarjejeniyar EU da Tunisiya kan 'yan gudun hijira

Mahmud Yaya Azare
June 13, 2023

Kasashen kungiyar tarayyar Turai sun cimma sabuwar yarjejeniyar sabunta matakan dakile kwararar bakin haure da Tunusiya wadda ta zama babbar kafar da masu fasa kwaurin bil adama ke bi zuwa Turai

https://p.dw.com/p/4SWlj
Tunesien Sfax | Europäische Spitzenpolitiker zu Gesprächen in Tunesien - Kais Saied
Hoto: Tunisian Presidency/ZUMA/picture alliance

A ziyarar tawagar Tarayyar Turai zuwa Tunusiya, dacta kunshi Firaministar Italiya Giorgia Meloni da Firaministan Nethalandas Mark Rutte da shugabar hukumar tarayyar Turai Ursula von der Leyen, ta nemi kasar Tuniya ta sake matsa kaimi wajen dakile kwarar bakin hauren da ke shiga nahiyar turai yayin da EU za ta bai wa  Tunusiya tallafin kudade masu yawa kamar yadda shugabar Tarayyar Turan Ursula von der Leyen ta baiyana.

Italien | Seenotrettung italienische Küstenwache
Hoto: Orietta Scardino/ZUMAPRESS/picture alliance

"Muna son kafa alaka mai karfi da kasar Tunusiya da zamu jima muna cin moriyar juna da tabbatar da tsaron kasashenmu gami da bunkasar tattalin arziki." 

A  bisa wannan yarjejeniyar, Tarayyar Turai za ta tallafa wa kasar Tunisia da kudade Euro biliyan daya da kuma karin euro biliyan daya da miliyan dari daya don biyan basuka a kasasfin kudin kasar Tunisia, sai dai za a tattauna wannan batun tare da dukkan kasashen kungiyar ta EU 27 don samun amincewarsu.

Bugu da kari, akwai batun tallafin euro miliyan 100 don tallafawa kasar wajen zamanantar da na'urorin hange nesa da fakon bakin haure, gami da saukaka ayyukan ceton gaggawa

Ursula von der Leyen da shugaba Kais Saied
Hoto: Italian Premier Office/AP/picture alliance

Shugaban kasar Tunisia Kais Saed, wanda kasarsa ke fama da matsalar tattalin arziki, yake kuma fuskantar kalubale daga hukumar IMF ya yi murna da tallafin wanda ya ce ya kamata a dinga bitarsa akai akai.

"Tun farko, mun yi koikari na radin kanmu wajen magance matsalar tattalin arzikinmu da hana kwararar bakin haure zuwa kasarmu, amma abun ya gagaremu. Don haka duk wani tallafin da zai taimaka na magance wadannan matsalolin abun a yi  maraba da shi ne.To sai dai hakan baya nufin zamu zama yan sanda ga Tarayyar Turai da za ta dinga keta hurumin bakin haure. Dola ne kamar yadda ake kokarin magance matsalar Tunusiya, su ma sauran kasashen da ke da irin wannan matsalar a mangance musu matsalolinsu tun daga tushe."

Kasar da ke yankin arewacin Afirka, wadda ke fama da matsanancin bashi kuma take kan tattaunawa don neman wani daga asusun bada lamuni na duniya IMF ta kasance mashiga ga bakin haure da masu neman mafaka da ke kokarin tsallaka wa Turai.