1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
Ta'addanci

Taron neman magance matsalolin tsaro

December 14, 2022

Ana ci gaba da shirya tarukan mahawara da zummar samo hanyoyin kawo karshen ta'addanci da masu garkuwa da mutane da satar dabbobi a Jamhuriyar Nijar musamman mazauna kan iyakar Katsina, Zamfara da Sokoto da ke Najeriya.

https://p.dw.com/p/4KuKN
Jamhuriyar Nijar
Matsalolin tsaro a Jamhuriyar NijarHoto: Kay Nietfeld/dpa/picture alliance

Wadanan taruka na Forum ko  mahawara da hukumomin jihar Maradi suka shirya a karamar hukumar Gabi da Gidan Sori sun hada wakilan bangarorin al'uma daban-daban da suka hada da sarakunan gargajiya, masu garuruwa,'yan sanda, 'yan majalisa, magajinan gari, kungiyoyin fararen fula da sauran masu ruwa da tsaki kan maganar tsaro na yankin gundumomi Madarounfa da Gidan Roumji. An kuma duba matsalolin tsaro a iyaka da Najeriya ta bangaren jihohin Katsina, Zamfara da Sokoto.

An dai shirya taruka da zumar samo sabbin shawarwari da dubaru na kawo karshen 'yan ta'adda da 'yan bindiga dadi masu garkuwa da mutane da satar dabbobin da ya zama ruwan dare a wannan yanki. Matsalar dai ta shafi kowa a cewar Gwamnan jahar Maradi Shaibu Abubakar.

Jamhuriyar Nijar | Gabanin ziyarar shugaban gwamnatin Jamus
Jamhuriyar NijarHoto: Kay Nietfeld/dpa/picture alliance

Tarukan forum na zuwa lokacin da hare haren da garkuwa da mutane ke dada zafafa tare da jefa alumomin yankunan cikin mawuyacin halin. Abu Mahaman wakilin hukumar karfafa zaman lafiya ta kasa HACP ya bayyana matsayi da shawara hukumar kan matsalar  tare da neman smaun taimakon duk bangarorin da suka dace.

Taron ya kuma ya tsaida muhimman shawarwaru da dubaru na bai daya da ke zaton idan an yi anfani da su cikin hikima to babu shakka matasalar za ta kau ko ta yi sauki.