1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mako na uku da barkewar rikicin Sudan

May 5, 2023

Bangarorin manyan hafsoshin sojan Sudan da ke kokowar karbe ragamar iko na ci gaba da gwabza fada ba tare da wasu alamu na tsagaita wuta ba, duk da kashedin da gwamnatin Amurka ta yi musu.

https://p.dw.com/p/4Qy97
Sudan | Kämpfe in Khartum
Hoto: AFP/Getty Images

Masu aiko da rohotanni sun ce a yayin da ake cika mako na uku da barkewar rikicin bangaron biyu sun yi ta barin wuta a wasu unguwanni na birnin Khartum da kuma kusa da filin sauka da tashin jiragen sama, duk da alkawarin da suka dauka na mutumta sabuwar yerjejeniyar tsagaita wutar da aka cimma har da wa'adinta zai kare a ranar 11 ga wannan wata na Mayu da muke ciki. Sai dai a ci gaba da rarrashin bangarorin biyu da kasashen duniya ke yi gwamnatin Masar ta ce ta tattauna ta waya da manyan hafsoshin sojan biyu, sannan kuma ministocin harkokin wajen kasashen Larabawa za su yi zama na musanman kan batun. A daya hunnun kuma sojojin da ke biyayya ga Janar Abdel Fattah al-Burhane sun sanar da nadin manzon da zai wakilce su a zaman sulhun da ake sa ran yi karkashi jagorancin shugabannin kasashen Sudan ta Kudu da Kenya da kuma Jibuti, sai dai har kawo yanzu ba a sanar da inda za a gudar da zaman ba.