1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sauyin sheka na 'yan siyasa a Najeriya

Uwais Abubakar Idris
February 17, 2022

A Najeriya ‘yan siyasa da dama na amfani da sauyin sheka daga jam'iyyar da suke zuwa wacce ke mulki don samun kariya daga zargin cin hanci da rashawa da suke fuskanta.

https://p.dw.com/p/47Aji
Najeriya I Zabe I Shugaban Kasa I 2019
Gabanin zaben 2023, 'yan siyasa na sauya sheka don gudun zargin rashawaHoto: Getty Images/AFP/L. Tato

Da zarar an shiga kakar zabe a Najeriya a kan ga ‘yan siyasa na ta zarya wajen chanza sheka musamman zuwa jam'iyyar da ke mulki a kasar bisa dalilai mabambanta, daya daga ciki shi ne kokari na samun kariya daga zargin da suke fuskanta na cin hanci da rashawa, inda wasu aka kai ga gurfanar da su gaban kotu. Sukan yi wannan da nufin a kawar da kai daga tuhumar da suke fuskanta sanin yanayi na rufa-rufa a gwamnati. 

Matsalar cin hanci da rashawa dai babba ce a tarayyar Najeriyar musamman a tsakanin ‘yan siyasa da ma ‘yan book da ke rike da amanara da aka basu ta dukiyar kasa, abinda ya sanya kungiyoyi da dama sa ido a kai. 

Kama daga gwamnoni zuwa sanatoci da ‘yan majalisar tarayya da ma ‘yan siyasar da basu  rike da mukami, ana ganin karuwar masu sauya sheka a Najeriyar, na baya-baya nan shi ne Sanata Emmanuel Bwacha  wanda ya bar PDP zuwa APC abinda wasu ke nuna yar yatsa bisa dalilai na neman kariya ne.

Da alamun dai ba'a kamala ganin masu sauya sheka ba a kakar siyasar da aka shiga yanzu a Najeriya sanin yadda jamiyyun ke  bullo da dubaru na kame madafan iko a kasar.