1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

CSC ta soke muhawara a Nijar

Gazali Abdou Tasawa LMJ
February 9, 2021

A Jamhuriyar Nijar Hukumar Kula da Harkokin Sadarwa ta Kasa wato CSC, ta sanar da soke muhawarar kai tsaye da ta nemi shirya wa a gidan talabijin na kasar tsakanin 'yan takarar shugaban kasar biyu.

https://p.dw.com/p/3p84k
Mahamane Ousmane 1995 Präsident Niger
Dan takarar jam'iyyar adawa a Jamhuriyar Nijar Mahamane OusmaneHoto: picture-alliance/dpa

Wannan mataki da Hukumar Kula da Harkokin Sadarwa ta Kasa a Nijar din wato CSC ta dauka dai, na zuwa ne bayan da dan takarar adawa Alhaji Mahaman Ousmane ya sanar da cewa ba zai halarci maBazoum Mohamedhawarar ba. Tuni kuma 'yan siyasa da ma sauran al'ummar kasar suka soma mayar da martani kan wannan batu. Hukumar ta CSC dai ta shirya gudanar da muhawarar ne a ranar 19 ga wannan wata na Fabarairu tsakanin dan takarar adawa Mahamane Ousmane da kuma na bangaren masu mulki Bazoum Mohamed.

Niger 's Innenminister Mohamed Bazoum
Bazoum Mohamed dan takarar jam'iyya mai mulki ta PNDS TarayyaHoto: Getty Images/K. Tribouillard

Sai dai da take mayar da martani, jam'iyya mai mulki ta PNDS Tarayya wacce dan takararta ya karbi gayyatar muhawarar daga hukumar ta CSC hannun biyu, ta bakin Malam Adamou Manzo ta ce ta san a rina domin a cewarsa dan takarar adawar ba ya da ta cewa a gaban al'umma.

Karin Bayani: Kaddamar da yakin neman zabe

Tuni dai matakin dan takarara adawar na Jamhuriyar Nijar na kauracewa muhawarar ya haifar da mabambantan ra'ayoyi daga al'ummar kasar, inda wasu ke ganin mutuncin da ke da akwai tsakanin 'yan takarar biyu da suka fito daga jiha daya ne, ya sanya dan takarar adawar ya nemi kauce wa duk wani sa in sa a bainar jama'a tsakaninsa da abokin hamayyar tasa wanda kane ne a gare shi ta wani fannin.