1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Dambarwar rikicin siyasa a Iraki

August 30, 2022

Kimanin mabiyan malamin 15 ne rahotanni ke cewa aka halaka a yayin arangamar da suka yi da jami'an tsaro a ranar Litinin a birnin Baghdad, lamarin da ya tunzura Moqtada al-Sadr fara yajin cin abinci.

https://p.dw.com/p/4GCZ9
Irak Muktada al Sadr
Hoto: Ali Najafi/AFP/Getty Images

Babban malamin shi'a na Iraki Moqtada al-Sadr ya fara yajin aikin cin abinci har sai jami'an tsaron kasar sun dakatar da abin da ya kira ''cin zarafi da amfani da makami a kan magoya bayansa''.

Tashin hankali dai ya biyo bayan furucin al-Sadr na janyewa daga harkokin siyasa a kasar da ke cikin rikicin shugabanci da kawo yanzu ba a tsayar da takamaiman shugaban kasa da firaminista ba.

Jim kadan bayan kalaman malamin, mabiyansa suka kutsa kai cikin gine-ginen gwamnati a yankin da ake yi wa lakabi da ''green zone'' mai matukar tsaro, inda suka fara artabu da jami'an tsaro.