1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Bukatar hana kyamar addini a duniya

Lateefa Mustapha Ja'afar
July 12, 2023

Kwamitin Kare Hakkin dan Adam na Majalisar Dinkin Duniya ya amince da matakin yin kira ga kasashen duniya, kan su kara kaimi wajen hana kyamar addini.

https://p.dw.com/p/4Tn4U
Majalisar Dinkin Duniya I Kwamitin Kare Hakkin dan Adam | Kyamar Addini
Taron kwamitin Kare Hakkin dan Adam na Majalisar Dinkin DuniyaHoto: Fabrice Coffrini/AFP

Wannan matakin da kwamitin Kare Hakkin dan Adam na Majalisar Dinkin Duniyar ya dauka yayin taronsa dai na zuwa ne, daidai lokacin da ake fuskantar kona al-Qur'ani a kasashen Turai. Kasashen Yamma dai sun nuna adawarsu da matakin, inda suka ce daukar tsauraran matakai a bangaren gwamnati ka iya yin illa ga 'yancin fadar albarkacin baki. An dai kaure da tafi a yayin taron, bayan da kasashe 28 mabobin kwamitin suka amince da matakin yayin da 12 suka kada kuri'ar kin amincewa bakwai kuma suka yi rowar kuri'unsu. Falasdinu da Pakistan ne dai suka kawo kudirin gaban kwamitin, yayin da suka samu goyon baya daga kasashe masu tasowa na Afirka da Chaina da Indiya da kuma kasashen yankin Gabas ta Tsakiya.