1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kokarin ceto daliban da aka sace a Kaduna

March 8, 2024

Gwamnatin jiar Kaduna ta sha alwashin kubutar da dukkan daliban da masu garkuwa da mutane suka yi awon gaba da su a Kuriga, a hannu guda kuma al'ummar garin na Kuriga ke ci gaba da kiraye-kirayen kubutar da 'ya'yansu.

https://p.dw.com/p/4dJyn
Najeriya | Kaduna | Dalibai | Tsaro
Al'ummar yankin Kuriga, sunyi dafifi cikin dimuwa da tashin hankaliHoto: AP/dpa/picture alliance

Kimanin yara 300 ne dai 'yan bindigar suka sace daga makarantunsu, tare da yin awon gaba da su a kan babura. Tuni dai gwamnatin jihar Kadunan ta baza jami'an tsaro a daukacin dajin da ke kewaye da yankin na Kuriga da ke yankin Arewa maso Yammacin Najeriya, domin ceto wadannan yara. Wannan dai shi ne sacta da kuma garkuwa da daliban na baya-bayan nan da ya afku a Kadunan, lamarin kuma da masu fafutuka ke dora alhakin faruwarsa a kan gawzawa ta fannin tattara bayanan sirri da kuma matsalar kai dauki a makare daga jami'an tsaro.

Najeriya | Kaduna | Dalibai | Tsaro
'Yan bindiga sun saba kai hare-hare, musamman a arewa maso yammacin NajeriyaHoto: Str/Getty Images/AFP

Tuni dai shugaban Najeriyar Bola Ahmed Tinubu ya yi tir da faruwar lamarin, cikin  wata sanarwa da fadar gwamnatin kasar ta fitar. Sanarwar ta nunar da cewa Tinibu ya ce ya samu  bayanai daga jami'an tsaro kan satar dalibai a jihohin Kaduna da Borno, wanda ya ce ya bayar da ummurni da a gaggauta ceton su. Tinubun ya kuma ya janjantawa iyalan wadanda abin ya shafa, yana mai ba su tabbacin cewar nan ba da jimawa ba za su sake haduwa da 'ya'yansu. Iyayen daliban da aka sace dai, sun shiga damuwa tare da fatan samun nasarar ceto su daga hannun 'yan binidgar. Sau da dama dai 'yan bindigar kasan sace mutane tare da yin garkuwa da su domin neman kudin fansa. Iyaye da al'ummar wannan yanki dai, sun yi fatan za a tabbatar da tsaro na din-din-din kasancewar ba yau aka soma ba.