1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hukumar yaki da cin hanci a Kano ta gayyaci Ganduje

Binta Aliyu Zurmi
July 6, 2023

Hukumar yaki da cin hanci a Kano ta gayyaci tsohon gwamna jihar Abdullahi Umar Ganduje a kan badakalar dala domin amsa wasu tambayoyi don wanke kansa.

https://p.dw.com/p/4TXPd
DW Karikatur Kano Nigeria Politik
Hoto: Mustapha Bulama/DW

Hukumar ta KPCACC a jihar Kano ta bayyana cewar za ta bi duk matakan da doka ta tanada a kan tsohon gwamnan Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje matukar ya bijirewa takardar sammacin da ta aika masa.

Hukumar na son tsohon gwamnan Kanon ya bayyana a gabanta dan kare kansa daga zargin karbar rashawa da ake yi mishi bayan ganin wani faifan bidiyo a shekarun baya.

Shugaban hukumar Barr Muhyi Magaji Rimin Gado, ya bayyana cewar suna sa ran tsohon gwamnan zai amsa gayyatar a makon gobe.

A shekarar 2017 ne aka fara sakin fefen bidiyon da ake zargin Ganduje ne yake karbar sunkin daloli yana cusawa a cikin aljihunsa, zargin da tsohon gwamnan ke musantawa ya na mai cewar fasahar zamani a kayi amfani da ita wajen kirkirar bidiyon.