1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Faransa ta sanar rufe masallaci mafi girma a birnin Paris

October 20, 2020

Wallafa faifan bidiyon jan kunnen malamin makarantar da aka hallaka a shafin facebook na wani masallaci a Paris kwanaki kalilan gabanin kisan da aka yi masa ya ja za a rufe masallacin.

https://p.dw.com/p/3kBYQ
Nach Ermordung eines Lehrers bei Paris Moschee Pantin Paris
Hoto: Christophe Archambault/dpa/picture alliance

A cigaba da binciken da hukumar 'yan sandan Faransa ke yi, bayan kisan da aka yi wa wani malamin makaranta a kasar wanda ya nuna hotunan batancin da aka yi wa manzon Allah ga dalibansa, ma'aikatar cikin gidan Faransa ta bayar da sanarwar rufe masallaci mafi girma a kasar daga gobe Laraba.

Rufe masallacin da ke gabacin birnin na Paris, ya biyo bayan wani faifan bidiyon jan kunnen malamin makarantar da aka wallafa a shafin masallacin na facebook kwanaki kalilan gabanin kisan da aka yi masa.

Masallacin mai yawan masallata dubu daya da dari biyar, zai kasance a garkame har na tsawon watanni shida ya yin da ake cigaba da bincike a cewar ministan harkokin cikin gida Gerald Darmanin.

Tuni dai rundunar 'yan sandan Faransa ta kaddamar da bincike tare da kamen mutane masu alaka da wasu kungiyoyin kishin islama.