1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ebola: Gini ta rufe iyakarta da Saliyo

Ahmed SalisuMarch 30, 2015

Gini ta sanar da rufe iyakokinta da kasar Saliyo na tsawon kwanaki 45 a wani mataki da ta ce ta dauka don dakile shigar cutar Ebola cikin kasar.

https://p.dw.com/p/1Ezn9
Afrika Ebola in Guinea (Symbolbild)
Hoto: picture-alliance/dpa/K. Palitza

To sai dai al'ummar kasar da dama sun koka game da wannan mataki da shugaban kasar Alpha Conde ya dauka a karshen mako don a cewarsu an shammace su kansacewar mutane da yawa sun ketare cikin Saliyo musamman Freetown, wanda rufe iyakokin ba zai bari su koma gida ba.

Wata mata da yaranta biyu da ke kokarin komawa Gini din daga Saliyo ta shaidawa kamfanin dillancin labarai na AP cewa jami'an tsaro sun hana su komawa gida Gini wanda hakan ka iya jefa su cikin matsala.

Dama dai a watannin baya Gini din kamar Saliyo da cutar ta Ebola ta yi wa ta'annaki ta dauki irin wannan matakin don magance yaduwar cutar daga yankunan da ta bulla a kan iyakokin kasashen biyu.