1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zargin tsohuwar ministar Najeriya da cin hanci

August 23, 2023

Hukumar yaki da manyan laifuka ta Birtaniya NCA ta sanar da cewa ana tuhumar tsohuwar ministar man fetur din Najeriya Diezani Alison-Madueke da aikata laifin cin hanci da karbar rashawa.

https://p.dw.com/p/4VT8L
Nigeria Diezani Alison-Madueke
Hoto: Joe Klamar/AFP

A sanarwar da ta fidda hukumar ta ce ana zargin Diezani Alison-Madueke da karbar cin hanci na tsabar kudi Fam dubu 100 da motocin hawa da tikiten balaguron shakatawa a lokacin da take rike da mukamin ministar mai fetur domin bayar da wasu kwangilolin makamashin Iskar Gas na makuddan kudade.

Karin bayani: Tsohuwar ministar man fetur  ta Najeriya na fuskantar tuhuma

Diezani wacce a halin yanzu ke zaune a birnin Landon za ta bayyana a gaban kotu a ranar biyu ga watan Oktoba mai zuwa domin wanke kanta daga wadannan zarge-zarge da ta dade tana musantawa.

Karin bayani: Najeriya: Kotu ta kwace kadarorin Diezani

Dama dai baya ga wannan laifi, ana zargin tsohuwar ministar da laifin halasta kudin haram a Amurka da Birtaniya da kuma Italiya, baya ga tuhuma kan laifin yunkurin karkata sakamakon zaben Najeriya na 2015 da hukumar EFCC ta yi mata.

Karin bayani: Najeriya ta tabbatar da tsare tsohuwar ministar harkokin man fetur din kasar.

Diezani Alison-Madueke mai shekaru 63 da haihuwa ta kasance kusa a gwamnatin Goodluck Jonathan tsakanin shekarun 2010 zuwa 2015, kuma ta rike mukamin shugabancin kungiyar kasashe masu arzikin man fetur ta OPEC.