1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Harin 'yan bindiga ya halaka mutane da dama

Abdullahi Maidawa Kurgwi SB/ATB
December 26, 2023

Jami'an tsaro a jihar Filato da ke Najeriya sun kaddamar da wani sabon farmaki don gano maharan da suka aikata harin da ya yi sanadiyar rasa rayukan mutane da dama a yankunan Bokkos, Mangu da Barkin Ladi da ke jihar.

https://p.dw.com/p/4aaWf
Jos fadar gwamnatin jihar Filato da ke Najeriya
Jos fadar gwamnatin jihar Filato da ke NajeriyaHoto: Kola Sulaimon/AFP/Getty Images

 

Tun dai a daren ranar Asabar da ta gabata ce aka soma fuskantar  hare haren yan bindiga a tsakanin  yankunan  na Filato  har zuwa  dare  jiya  Liktin,  kuma wani mazaunin yankin gundumar Mbar, da ke karamar Bokkos, Edward Silas wanda tsohon Kansila ne a yankin, ya shaida cewar hare-haren 'yan bindiga sun yi sanadiyar mutuwar mutane da dama, kuma wasu daruru sun sami raunuka inda yanzu haka suna kwance a asibitoci suna jiyyar raunuka da suka samu.

Kabin Bayani: An tabbatar wa PDP kujerar gwamna a Filato

Jihar Filato da ke Najeriya inda ake samun tashe-tashen hankula irin na addini
Jihar Filato da ke NajeriyaHoto: picture-alliance/dpa

Babu bayanai na alkaluma a hukumance kan adadin mutane da suka rasa rayukansu sanadiyar hare-haren 'yan bindiga wanda wasu ke zargi Fulani ne da aikatawa, to amma ta wayar tarho shugaban kungiyar Miyetti Allah na jihar Filato, Nura Abdullahi ya ce  Fulani  sun yi hasarar rayuka a hare-haren na 'yan bindiga.

Wani Manomi da ke yankin  Mr Danjuma Mabas ya shaida cewar mutanenn Barkin Ladi da Mangu ma hare-haren ya shafe su to amma lamarin yafi kamari ne a karamar hukumar Bokkos inda yanzu haka suke kokarin binne mutanen da lamarin ya shafa.

Komandan rundunar da ke wanzar da zaman lafiya a jihar Filato Manjo Janar  Abdulsalam Abubakar ya yi alwashin zakulo mutanen da ke da hannu a wannan aika-aikar. A wani jawabi da ya gabatar jim kadan bayan taron majalisar tsaro ta jihar Filato, Manjo Janar Abdulsalam Abubakar ya bayyana cewar sun gano wasu daga irin kayyayakin da maharan suka yi amfani da su lokacin da suke  kai harin. Yanzu haka dai ana zaman zullumi da alhini a yankuna da maharan suka yi  wa kawanya a 'yan kwanakin nan.