1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An fasa tafiya yajin aiki a Najeriya

September 28, 2020

Kungiyoyin kwadago a Najeriya sun dakatar da yajin aikin gama-gari da suka shirya farawa a fadin kasa a ranar Litinin, bayan cimma daidato da suka yi da gwamnatin kasar.

https://p.dw.com/p/3j5NZ
Demonstration gegen Strompreis-Anstieg in Nigeria
Hoto: picture-alliance/dpa

Kungiyoyin dai sun tsara yajin aikin ne saboda turje wa gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari, wadda ta dauki matakin janye tallafi kan makamashin man fetur da na wutar lantarki, abin da ya janyo tsanantar halin rayuwa a Najeriyar a yanzu.

A makon jiya ne babbar kungiyar kwadago ta NLC da ke wakiltar miliyoyin ma'aikata a kasar da ta fi kowacce karfin tattalin arziki a Afirka, ta sanar da shirin fara yajin aikin a yau Litinin.

Shugaban Najeriyar Muhammadu Buhari, ya ce kasar ba za ta iya ci gaba da biyan tallafin ba, dole ne a bar kasuwa ta yi alkalanci, amma kungiyar kwadagon ta kekashe kasa ta ce lallai ne a dawo da farashin mai da wutar lantarki, muddin hukumomin na son sansatawa da ita a kan yajin na aiki.