1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An kawo karshen zanga zanga a Kashmir

Abdullahi Tanko Bala
May 14, 2024

Gwamnatin Pakistan ta sanar da tallafi domin saukar da farashin fulawa da wutar lantarki bayan shafe kwanaki hudu ana zanga zanga da ta yi sanadiyar mutuwar mutane hudu yayin arangama da yan sanda.

https://p.dw.com/p/4fr1r
Jana'izar mutanen da suka rasu a zanga zangar Muzaffarabad a Kashmir
Jana'izar mutanen da suka rasu a zanga zangar Muzaffarabad a KashmirHoto: Sajjad Qayyum/AFP

Masu zanga zanga a yankin Kashmir da ke karkashin ikon Pakistan sun dakatar da gangamin da suke yi bayan da wadanda suka shirya zanga zangar suka amince da  tayin tallafi da kuma rage farashin kayayyaki da gwamnati ta yi musu.

Pakistan da Indiya kowannensu na iko da wani bangare na yankin na Himalaya amma kuma suna ikrarin dukkan yankin na su ne.

Yankin ya kasance abin da ya dade yana haifar da takaddama tsakanin kasashen biyu da suka mallaki makamin nukiliya wadanda kuma suka gwabza yaki da juna har sau uku akan yankin.

Yankin Kashmir da ke karkashin iko Pakistan ya kasu zuwa rassa uku masu kwarya kwaryar cin gashin kai wadanda a hukumance ake kira Azad Kashmir da kuma yankin da ke karkashin ikon tarayya mai suna Gilgit-Baltistan.